27 AMINIYA Juma’a, 2 ga Janairu, 2015 SIYASA Yanzu ba a sayen mutane a siyasa – Mace ’yar takarar Gwamna Sanata A’isha Jummai Alhassan Sanata ce daga Jihar Taraba, kuma a halin yanzu ita ce mace ’yar takarar Gwamna a Jihar Taraba a qarqashin Jam’iyyar APC. A wannan tattaunawa da ta yi da Aminiya ta yi bayanin dangantakarta da xan takarar Shugaban Qasa a Jam’iyyar APC Janar Buhari da kuma dambarwar siyasar da ke gudana a Jihar Taraba. Ga yadda hirar ta kasance: Daga Magaji Isa, Jalingo Aminiya: Ana raxe-raxin cewa akwai rashin jituwa tsakaninki da xan takarar Shugaban Qasa na Jam’iyyar APC Janar Muhammadu Buhari, mene ne gaskiyar wannan lamari? A’isha Alhassan: Wannan ba gaskiya ba ne, akwai kyakkyawar fahimta tsakanina da Janar Muhammadu Buhari, domin duk lokacin da na haxu shi nakan durqusa in gaishe shi. Bari in faxa maka, duk lokacin da shi Janar ya gan ni abin da yake fara kirana da shi shi ne “Gwamnata,” kafin ma mu soma gaisuwa. Ni kuma sai in ce lafiya lau Sa, saboda haka akwai kyakkyawar fahimta tsakanina da Janar Buhari. Kuma siyasa ba yaqi ba ne ko kuma abin gaba, duk da kasancewar ban yi shi ba a lokacin zaven fidda xan takarar Shugaban Qasa na jam’iyyarmu ta APC da aka gudanar a garin Legas, amma Janar Buhari bayan mun dawo daga Legas ya tafi gidan xan takarana Alhaji Atiku Abubakar a Abuja ya gode masa ya kuma nemi haxin kansa. Ni ba ni da wani abu a zuciyata, wato ba ni da wata qullaliiya ko gaba da Janar Muhammadu Buhari. A zaven shekarar 2011 ina cikin Jam’iyyar PDP, amma Janar Buhari na zava, saboda wani dalili na qashin kaina. Aminiya: To me ya kawo wannan zargin? A’isha Alhassan: Wannan aikin jahilan ’yan siyana ne waxanda ke yin gaba da waxanda ba su zavi wani xan takara ba. In ban da jahilci, ya kamata a ce daga ranar da aka zavi Janar Buhari a matsayin xan takarar Shugaban Qasa, to a ce babu sauran maganar ofishin kamfen na Janar Buhari. Abin da ya kamata shi ne, a maida hankali wajen gudanar da kamfen don ganin Janar Muhammadu Buhari ya samu nasara, ba wai ka-ce-na-ce ba, kamar abun da ke faruwa a Jihar Taraba. Saboda haka idan su jahilan ’yan siyasa ne shi Janar n Sanata A’isha Jummai Alhassan Buhari ba jahilin xan siyasa ba ne.Kuma ya kamata jama’a su san matsayina a kan Janar Muhammadu Buhari, shi uba ne a gare ni, kuma shi ne xan takarar Shugaban Qasa na jamiyyarmu. Zan bayar da gudunmawata ga kamfen xinsa domin ganin Janar Buhari ya lashe zave saboda in qara jaddada cewa ba ni da wata matsala da Janar Buhari, yana goyon bayana, ni kuma ina goyon bayansa. Aminiya: Wasu mutanen ofishin kamfen na Janar Buhari a Jihar Taraba sun ce ba a yi zaven gaskiya ba a lokacin da aka zave ki a matsayin ’yar takarar Gwamna na Jam’iyyar APC a jihar. Me za ki ce? A’isha Alhassa: Idan za a yi zaven fidda da xan takarar Gwamna a Jam’iyyar APC a Jihar Taraba sau xari zan lashe zaven. Duk wanda ya kasance a inda aka gudanar da zaven fidda xan takarar Gwamna na jam’iyyarmu ta APC a Jalingo ya san cewa zave ne na gaskiya aka yi, ba wai xauki xora ba, babu wani maguxi, ko faifan bidiyo na zaven yana nan, saboda haka ba a voye aka yi wannan zave ba. Kamar yadda kowa ya sani, kowane wakili ya kaxa quri’arsa a lokacin zaven , waxanda suka faxi zave ne suke irin waxannan maganganu marasa tushe domin su kawo ruxani a tafiyar da muke yi. Ya kamata irin waxannan mutane su sani cewa yanzu an daina siyasar kuxi. Waxannan ’yan takara da ba su yi nasara ba, ba sa tare da jama’a. Sun daxe ba su zo Jihar Taraba ba, sai kawai da zave ya qarato suka shigo Taraba, akwai wani xan takara ma kwana huxu kacal ya rage a yi zave ya shigo garin Jalingo. Yanzu ba a sayen mutane a siyasa, mutane suna tare da wanda yake tare da su ne, ba wai kawai sai lokacin zave mutum ya xauko kuxi ya ce yana neman ya sayi jama’a ba. Abin da ya kamata waxannan ’yan siyasa su yi shi ne su natsu su gano inda suka yi kuskure su gyara don gaba. Amma sun kasa yin haka sai surutan banza. Ina qara nanata cewa idan za a yi zaven fidda ’yan takara sau xari zan yi nasara, domin ina tare da mutane, mutane suna tare da ni. Waxansu daga cikin waxanda suka faxi zave sun raba kuxi, amma an qi zavensu, daga cikinsu akwai waxanda suka bayar da Naira dubu talatin da biyar, waxansu kuma sun bayar da Naira dubu ashirin da biyar, amma an qi zaven su domin ba sa tare da jama’a. Aminiya: Ana zargin cewa qafarki xaya na cikin Jam’iyyar APC ne xaya kuma na cikin Jam’iyyar PDP, haka ne? A’isha Alhassan: Ana yin wannan zargin ne don na je taryar Alhaji Sani Abubakar Xanladi a lokacin da ya iso Jalingo bayan Kotun Qoli ta bayar da umurnin cewa a maida shi kan muqaminsa. Tun kafin a tuve shi akwai kyakkyawar dangantaka tsakanina da shi, kuma a da can a Jam’iyyar PDP muke, sannan a lokacin da na tsaya takarar Sanata na mazavar Taraba ta Tsakiya ya taimaka mini na ci zave. Abu na biyu shi ne, xaya daga cikin dalilan da Xanbaba Suntai ya kawo don a tsige Alhaji Sani Xanladi shi ne, wai ni da shi da Sanata Tutare Abubakar mun haxu mun kitsa yadda za mu kashe shi Xanbaba Suntai a lokacin da muka tafi aiki Umara a qasar Saudiyya. A zahirin gaskiya ba mu haxu da Sani Xanladi a qasar Saudiyya ba, domin a ranar da na bar qasar Saudiyya a ranar ce shi kuma Sani Xanladi ya isa qasar. To, ganin dukkan dalilan da aka bayar a matsayin hujjar cire Alhaji Sani Xanladi duk qarya ne, sai na kira ’yan majalisar Jihar Taraba xaya da xaya na ba su shawarar cewa wannan abin da suke so su yi, ba gaskiya ba ne, kuma zai iya kawo rigima a jihar, amma suka qi jin shawarata. Kowa ya san cewa ba a bi gaskiya ba wajan tsige Alhaji Sani Abubakar Xanladi. Bayan wannan kuma lokacin da ya yi gudun hijira ya zo Abuja, yakan zo ya gaida da ni, ni ban kashe ko kwabo a wajen shari’arsa ba, amma na taya shi addu’a wajen ganin Allah Ya taimake shi ya samu haqqinsa da aka tauye ta hanyar tsige shi da aka yi ba a kan qa’ida ba. Sannan kuma ya kamata ka fahimce cewa an yi haka ne don wanda aka tsige a kan muqaminsa a shafa masa kashin kaji a hana shi ya tsaya takara har sai bayan shekara goma. Kamar yadda na faxi tun farko cewa akwai fahimta kyakkyawa a tsakanina da shi, saboda haka ashe bai zama laifi ba, idan na taya wannan mutum murna bayan ya samu nasara a kotu. Ya kamata kowa ya san cewa, in don na je taryar Alhaji Sani Xanladi shi ne laifi, to na yi laifin kuma Alhaji Sani Xanladi ya dawo Jihar Taraba a matsayin Mataimakin Gwamnan Jihar Taraba, kuma ni Sanata ce wadda ke wakiltar mahaifarsa, saboda haka ban ga wani laifin yin haka ba.
© Copyright 2024