Zinariya 23 AMINIYA Juma’a,2 ga Janairu, 2015 Sanyin idon kowace mace IYAYEN GIJI Mata da cututtukan zamani Abubakar Haruna, Daga Legas A ci gaba da nazari da muke yi a kan mata da cututtukan zamani a wanannn mako za mu dubu yadda jahilci da kunya ke sanyawa mafi yawan mata suke faxawa cikin tarkon kamuwa da cututtuka masu yawa a wannan zamanin da muke ciki. Da dama daga matanmu sun jahilci yadda ake kamuwa da irin waxannan cututtuka, kamar cutar sanyi irin su gonoriya da tsargiya da yankan gashi da sauransu, waxanda suke haddasa qaiqayin gaba da quraje da fitar ruwa daga gaban mace ko namiji da wari farjin mace da savar azzakari da qanqacewar azzakari da kumburin farji da azzakari da sauran su. Babu shakka mafi yawan mata sun kamu da irin waxannan cututtuka, amma sai kunya ta hana su bayyanawa don a nema musu magani. Idan matar aure ce sai ka ga ta voye wa mjinta don jin tsoron kada ya zarge ta da fasiqanci, idan kuwa budurwa ce sai ita ma ta voye wa saurayin da zai aure ta saboda tsoron sakamakon abin da zai haifar. Ba komai ke janyo wa mata suke voye kamuwa da cututtukan ba sai tsabar jahilci, domin idan da sun san haxarin barin cutar a jikin xan Adam da sun yi gaggawar bayyanawa domin a gaggauta nema musu magani. Wani abin mamaki shi ne za ka ga yarinya budurwa tana fama da irin waxannan cututtuka, amma sai ka ga ta voye wa mahaifiyarta duk da irin shaquwar da suka yi. Haka za a yi mata aure ba tare da sanin iyayenta ba ko saurayin da ya aure ta, sai daga bisani idan mijin ya kamu a riqa kame-kamen yadda za a yi maganin abin. Wata kuwa saboda tsabar jahilci sai ta riqa bin qawayenta tana gaya musu tana tsammanin za su taimaka mata, amma daga bisani sai su ci amanarta su riqa yaxa ta a duniya har ya kai idan wani saurayi ya fito zai aure ta su gaya masa cewa tana da ciwon sanyi. Shi ya sa shawarar da nake bai wa mata ita ce duk lokacin da suka DUNIYAR MA’AURATA fahimci sun kamu da xaya daga cikin waxannan cututtuka, to su natsu, kada su tayar da hankalinsu, su tafi asibiti kai tsaye a auna su a tabbatar da irin dangin ciwon sanyin da yake damun su, ta yadda za a san maganin da za a ba su. Wannan shi zai sanya su ma su san irin nau’in cutar sanyin da take damun su. Wani abin lura shi ne babban dalilin da ya sa wasu matan suke voye cutar shi ne gudun tsangwama daga waxanda ke tare da su, kamar iyaye da ’yan’uwa. Don mafi yawan jama’armu idan aka yi zancen ciwon sanyi abin da suke fara tunani shi ne, mutum ya xauka ne ta hanyar banza kamar jima’i. Tare da Nabeela Ibrahim Khaleel Tambayoyin Duniyar Ma’aurata 7 Assalamu Alaykum wa rahmatullahi wa barakatuh. Barkanmu da sake haxuwa cikin wannan fili, da fatan Allah Ya amfanar da mu dukkan bayanan da za su zo cikinsa, amin. Ga ci gaba akan amsoshin tambayoyin da masu karatu suka aiko, da fatan Allah yasa wannan bayani ya isa ga duk masu buqatarsa, musamman waxanda suka aiko da tambayoyin, amin. T ambaya Ta 17: Na ji kun ce Mala’i’ku ba su shiga gidan da yake da hoto, wane irin hoto ke nan, hoton Maigida da Iyalansa? Ina neman qarin bayani. Amsa: Annabi SAW ne ya faxi haka; cewar Mala’iku ba su shiga gidan da cikinsa akwai hoto, zane ko taswirar dukkan wani abu mai rai. Wannan ya zo a cikin ingantaccen Hadisin da aka ruwaito daga Uwar Muminai Aishah RA. Amma ba laifi akan hotunan furanni da shuke-shuke. Tambaya Ta 18: Ina tambaya ne game da amfani da baki wajen ibadar aure: Kun ce waxansu Malamai sun ce ba haramun ba ne, sai dai in maniyyi ko maziyyi ya shiga baki sannan ya zama haram. Shin sai an haxiye ne ko kuma a baki kawai? Domin waxansu sun ce sai an hadiye ne zai zama haram; don Allah ina son qarin bayani. ---Dahiru Umaru. Amsa: Kamar yadda bayani ya gabata cewa, wani vangaren na Malamai na xaukar maniyyi da dangoginshi a matsayin qazanta kawai (watau khaba’ith). Shigar maniyyi da dangoginsa cikin baki haramun ne, domin su xin abubuwan qazanta ne, bakin xan Adam kuwa ba wurin sanya abubuwan qazanta ba ne, don haka ba inda shari’a ta amince da shigar abin qazanta cikin baki. Allah SWT ya haramta mana ci ko shan abubuwan qazanta a cikin Al’qur’ani Mai girma; misali, a cikin Aya ta 157 cikin Suratul A’araf: “Kuma Shi (Allah Maxaukaki) Ya haramta musu abubuwan qazanta…” Don haka dole ma’aurata su kiyaye kar waxannan abubuwa suna shiga cikin bakunansu, har in ya zamar musu dole sai sunyi haka xin; da fatan Allah Ya bada ikon kiyayewa, amin. Tambaya Ta 19: Ina so ku gaya min yadda zan shawo kan Maigidana don ya rinqa dawowa gida da wuri. Amsa: Ga shawarwarwarin duniyar ma’aura gareki: 1. Abu farko shi ne ki yi haquri, kuma ki qara ba kanki haquri; ki sani kowane xan Adam yana da wasu buqatu da uzurorin da suka sha bamban da na wani xan Adam xin; kuma waxanda sun riga sun rikixe da xabi’unsa, ta yadda zai yi wuya ya iya rabuwa ko daina aikata su farat xaya komin yadda aka so haka xin. Don haka kyakykyawan haquri, shi ne magani na farko. 2. Addu’a tana maganin dukkan matsalolin rayuwa; don haka sai ki dage da yi masa addu’a a kowane lokaci, kum musamman a lokuttan amsar addu’a: kamar cikin sujjudar Salloli da lokacin zaman tahiya kafin sallama da ranar Juma’a bayan Sallar La’asar da sauransu. Sannan ki dage wajen tsaidawa da kyautata ibadarki da yawan yin nafiloli, musamman na azumi da tsayuwar Saboda haka ya kamata jama’a su daina ruxewa don sun kamu da wata cuta, abin da ya kamata mutum ya yi shi ne, ya tafi asibiti a auna shi, a tattabar da nau’in cutar, kuma ya nemi maganin bature, idan na bature bai karve shi ba, to ya gwada na musulunci ko na gargajiya. Da yardar Allah zai samu lafiya. Amma kuma ya kamata mutane su riqa kiyaye hanyoyin da ake xaukar waxannan cututtuka kuma su tsare kansu da iyalensu sannan kuma a guji jita-jita. Abubakar Haruna ya rubuto daga Legas 08027406827 abubakarharuna2003@ gmail.com. [email protected] 08063675635 (TES KAWAI): Facebook/Duniyar Ma’aurata dare, in sha Allahu za ki samu biyan buqatarki. 3. Ki sani, mafi yawa daga mazaje sun fi son zaman waje akan zaman cikin gida, wannan wani abu ne da ya samo asali daga ainihin gundarin halayyar xa namiji. Don haka in dai ba wani aikin ashsha ne yake sa shi daxewa a waje ba, to ki yi haquri, ki bi shi a hankali har Allah Yasa ya rage daxewa a waje sosai. 4. Ki daina jin haushin mijinki saboda wannan xabi’a akan wannan xabi’a da yake yi da baki so, matuqar kina jin haushin abin, kuma kina bayyanar masa da jin haushin, to wannan ba zai sa ya daina ba, sai dai ya qara ingiza shi ma ga aikatawa. 5. Kar ki rinqa yawan damunsa da mita da qorafin bai dawowa da wuri, in zai tafi ki yi masa rakiya, kina mai masa addu’ar Allah Yasa a dawo lafiya cikin sakin fuska da annashuwa. In ya dawo kuma ki tarbe shi cikin sakin fuska da annaashuwa, tare da gabatar masa da dukkan abin da kika san yana buqata a wannan lokaci. 6. Ki binciki kanki da yanayin zaman ku da shi bincike mai zurfi, wataqila akwai wani abu da kike yi masa wanda yasa bai son zaman gida, kamar in kina damunsa da yawan mita da qorafi, ko ba ki gyara gidan ki ko yanayin yadda gidan yake ne yasa bai son zama, duk abin da kika lura yana da nasaba da matsalar sai ki yi dukkan qoqarin da ya kamata ki ga cewa wannan abin ya daina faruwa. 7. Ki duba cikin ma’ajiyarki ‘yammatacinki, ki binciko hanyoyin qayatarwa da nishaxanwar da za ki rinqa gabatar masa, ta yadda zai ji bai ma son fita wajen ya fi son kasancewa tare da ke. Sai mako na gaba in sha Allah, da fatan Allah Yasa mu kasance cikin kulawarsa a koda yaushe, amin.
© Copyright 2024